Tsokaci Kan Sabuwar Dokar Ta’ammali Da Kafafen Sadarwa na Zamani a Najeriya (1)

Manyan al’amuran da wannan doka ta shagaltu dasu dai guda biyu ne: na farko shi ne ayyukan dukkan kafafen sadarwa na zamani dake Intanet, wadanda ‘yan Najeriya ke amfani dasu; suna da rajista ne, ko babu rajista.  Wadannan kafafe kuwa, kamar yadda na ayyana a baya, su ne kafafen sada zumunta, irin su Facebook, da Twitter, da Google (Youtube), da WhatsApp (Facebook/Meta), da kuma dukkan jami’ai ko wakilansu a Najeriya.  Sai abu na biyu, wato tabbatar da hanyoyin kariya ga ‘yan Najeriya da ma baki, a kafafen sadarwa na zamani. – Jaridar AMINIYA, Jumma’a, 1 ga watan Yuli, 2022.

Karin Bayani...

Sakonnin Masu Karatu (2022) (3)

A duk sadda ka matsa alamar “Like” dake wani shafi (Page), ko karkashin wani rubutaccen sako (Text Post), ko hoto (Image Post), ko bidiyo (Video Post), za a wallafa sunanka a jerin wadanda suka ga wannan sako, kuma suka nuna sha’awarsu gareshi.  Sannan wannan zai sa injin Facebook ya yi hasashen nuna maka wasu sakonni masu alaka da wanda ka kaunata.  Wannan ke tabbatar da tasirin wannan alama ta “Like”! – Jaridar AMINIYA ta ranar Jumma’a, 29 ga watan Afrailu, 2022.

Karin Bayani...

Sakonnin Masu Karatu (2022) (2)

Dandalin Facebook ya samar da wani tsari da ke baiwa mutane damar rufe shafinsu da zarar sun rasu.  Galibi an fi amfani da wannan tsari a kasashen da suka ci gaba.  Dangane da haka, da zarar wani ya mutu, kuma ‘yan uwansa suka sanar da hukumar Facebook, nan take za a cire shi daga adadin wadanda suke bibiyar kowane irin shafi ne ko dandali.  – Jaridar AMINIYA ta ranar 22 ga watan Afrailu, 2022.

Karin Bayani...