Sakonnin Masu Karatu (2012) (7)

Ci gaban sakonnin masu karatu.  A sha karatu lafiya.

71

Assalaamu Alaikum Baban Sadik, ina fatan kana tare da iyalanka gaba daya lafiya.  Hakika ka yi tsokaci a kan abu mai mahimmanci wanda ya dade yana damu na kuma yake halaka samarinmu, a makalarka mai taken: “Rayuwar Matasanmu a Dandalin Facebook.”  Mun ji dadin wannan bayani naka, Allah ya biya ka.  Don bayan wannan bayani naka da mako daya sai ga shi an samu mace da namiji matattu a mota a Kano, kuma duk ta sanadiyyar soyayyar Facebook ne.  Sai dai ka yi bayanin cuta amma baka fadi magani ba.  Don Allah kayi magana a kan abubuwan da suka kamata matasa su mayar da hankalinsu a kai a Dandalin Facebook.  Na gode.  Yusuf Mu’azu, ABU Zaria: 08031802438

Wa alaikumus salam, Malam Yusuf na gode da wannan tsokaci da ka yi kan wancan makala, duk da cewa ban gama da wannan maudu’i ba.  Kashin farko ne na fitar, kuma zan ci gaba in Allah Ya yarda.  Dangane da hanyoyin da suka kamata a bi wajen magance ire-iren wadannan abubuwa, ai na fadi wasu daga ciki a karshen makalar, watakila hankalinka bai kai kan bayanin bane shi yasa.

- Adv -

Zan ci gaba da wannan silsila har sai illa ma sha’Allahu.  Zan kuma gabatar da wata silsilar kan hanyoyin da suka kamata mu rika shagaltar da kanmu don samun ci gaba a Intanet ma gaba daya, ba wai Dandalin Facebook ba kadai.  Sai dai dole ne ka san cewa shi gyara wani abu ne da ke daukan lokacin kafin tasirinsa ya fara bayyana.  Allah sa mu dace baki daya, amin.


Assalaamu Alaikum Baban Sadik, ina fatan kana lafiya.  Na ji dadin rubutun da kayi na “Tsarin Gadon Dabi’u da Siffofin Halitta.”  Allah Ya kara maka basira, amin.  daga Alhaji Ibrahim: 08030840905

Wa alaikumus salam, Alhaji Ibrahim barka da warhaka.  Na gode da wannan sako naka. Allah saka da alheri amin.  Kamar yadda ka karanta, wannan kasida yanzu muka faro ta. Sai a ci gaba da kasancewa tare da mu.

- Adv -

You might also like
Leave A Reply

Your email address will not be published.