Sakonnin Masu Karatu (2011) (20)

Wadannan sakonnin tsokaci ne da wasu cikin masu karatu suka rubuto.  Sakon a fili yake, ba ya bukatar karin bayani ko wata amsa.

85

Baban Sadik Allah ya kara basira.  Na ji dadin wannan bayani.  Zan kira shi “Mabudin Ilmi.” Hakika duk ilmin da ba imani, da sanin mahalicci, da yarda da dokokinsa, da aiki da shi a cikinsa, to bata ne.  A huta lafiya.  –  Mustapha, Kofar Nasarawa, Kano: 08052228790


- Adv -

Assalaamu Alaikum, na ji dadin bayananka kan addini.  A “Kundin Gwamna Lugga” shafi na 131 da 135, akwai tsokaci game da karatun boko, (cewa):  “Dole ne mu tsaya mu ga an koyar da duk wani abu na kyautata halayen yara da ke makarantu, domin su zama masu alkunya da sanin ya kamata. Ba wai a yi ta ba yara ilmi kawai ba, satata babu kyawawan halaye.  Dole ne Gwamnati ta tsaya tsayin daka ta ga an samar wa addini gindin zama.” 

A shafi na 135 kuma ya sake cewa: “Mai hankali hattara yake yi da abin da ya samu waninsa. (Tsantsar) karatun boko ya jawo tsiya, da bala’i, da tajrifi a kasashe kamar Hindu, da Sin, da nahiyar Afirka, a sanadin bokon da ba a gauraya shi da addini ba.  Duk wanda ya yi bokon da ba addini, to ya shiga uku, domin ba zai girmama iyayensa ba balle magabatan garinsu.  Shi kansa ma ba zai iya yi wa kansa abin alheri ba.  Wannan yana daga cikin abin da Lugga ke baiwa ma’aikatansa a cikin kundinsa mai suna: “Political Memoranda.”  – Mahfouz Tasiu Abdullahi, Kano: 08026506085

- Adv -

You might also like
Leave A Reply

Your email address will not be published.