
Kwarewa a Fannin “Computer Science”
Wannan kashi na uku kenan cikin fadakarwar da muka faro a makon jiya kan hanyoyin da mai karatu zai iya kwarewa a fannin kimiyya da fasahar sadarwa na zamani. A yau mun dubi fannin “Computer Science” ne.
Makaloli a fannin kimiyya da fasaha!
Wannan kashi na uku kenan cikin fadakarwar da muka faro a makon jiya kan hanyoyin da mai karatu zai iya kwarewa a fannin kimiyya da fasahar sadarwa na zamani. A yau mun dubi fannin “Computer Science” ne.
Daga wannan mako in Allah Yaso, za mu fara fadakar da masu karatu kan fannonin da mutum zai iya kwarewa a kai cikin fannin kimiyyar fasahar sadarwa na zamani, wato “Information Communications Technology.” Kasidar yau dai gabatarwa ce. A sha karatu lafiya.
A yau za mu karasa bayani kan sauran shahararrun manhajojin da suka ci duniya (kuma suke kan ci a yanzu) a duniyar Intanet, wajen aiwatar da wadannan aikace-aikace na cutarwa. Sai dai kuma, sabanin yadda nace a makon da ya gabata, ba za mu iya karkare bayanai cikin wannan mako ba, sai zuwa makonni uku nan gaba in Allah Ya yarda.
Idan mai karatu na tare da mu, muna yin bayani ne kan kwayoyin cutar kwamfuta da illolin su da kuma masu hakki wajen kirkiro wannan annoba. Har wa yau, a makon da ya gabata mun kawo bayanai kan tsarin da masu wannan al’ada ke bi wajen yada kwayoyin cutar da ke ma kwamfuta illa a duniya. A karshe kuma mai karatu ya samu bayanai kan tasirin wannan sana’a nasu, hatta ga siyasar duniya. A yau za mu ci gaba, inda za mu kawo hanyoyin da wadannan masana harkan kwamfuta ke bi wajen shiga kwamfutocin jama’a; ko dai don yada kwayoyin cuta, ko aiwatar da satan bayanai, ko kuma don sace ma jama’a kudade da kuma aikin leken asiri.
Wannan ci gaba ne daga kasidar da ta gabata a makon jiya, kan yaduwar harshen Hausa a Intanet, da irin huldodin da al’ummar Hausawa ke gudanarwa a Intanet.
A wannan za mu dubi yaduwar harshen Hausa ne a Intanet, da sadda wannan fasaha ta iso Najeriya da kuma wadanda a farkon lamari suka fara alaka da wannan fasaha a al’ummar Hausawa.
A yau za mu dubi fasahar sadarwa ta Rediyo ne a Intanet. A baya masu karatu sun karanta kasidar dake bayani a kan kafofin sadarwa a Intanet, inda muka tattauna kan samuwar jaridu, da talabijin da kuma rediyo. A wannan karo za mu dubi fasahar rediyo ne don kara fahimtar hakikanin yadda take gudanuwa.
A makon da ya gabata ne idan masu karatu ba su mance ba, mu ka fara jero bayanai kan irin tasirin da Fasahar Intanet ke yi ga kwakwalwar dan Adam, saboda irin mu’amalar da ya ke yi da wannan fasaha. Mun yi bayanin irin dalilan da ke haddasa tasirin, da kuma cewa lallai akwai alaka tabbatacciya mai kama da kawalwalniya, wacce ke samuwa tsakanin kwakwalwar dan Adam da kuma asalin duniyar da yake ciki. Mun nuna cewa wannan alaka na samuwa ne sanadiyyar tasirin wannan fasaha da kwakwalwar mai mu’amala. Daga karshe mu ka yi alkawarin kawo abin da hakan ke haifarwa, da yadda za a iya magance wata matsala idan akwai. Saboda yanayin tsarin da bayanan su ka zo, mun ce mai karatu ba zai fahimci in da aka dosa gaba daya ba, sai a wannan mako. Mu na kuma fatan hakan. Don haka yanzu za mu ci gaba.
Tsarabarmu na wannan mako kan tasirin fasahar Intanet ne ga kwakwalwar dan adam. A sha karatu lafiya.
An samu kari daga cikin kamfanonin sadarwa na wayar salula masu lasisi a kasarmu Najeriya. Amaryar da muka yi ita ce: “Etisalat”, daya daga cikin manyan kamfanonin sadarwa da ake ji dasu a kasashen larabawa.
Ga kashi na hudu cikin jerin kasidun dake mana bayanin tsari da yadda aka gina manhaja da shafukan Dandalin Facebook. A sha karatu lafiya.
Ga kashi na uku cikin jerin kasidun dake mana bayanin tsari da yadda aka gina manhaja da shafukan Dandalin Facebook. A sha karatu lafiya.