Gaskiya da Gaskiya (4): Neman Zabin Allah…!
A duk abin da za kayi, wanda halal ne gareka, amma baka san yadda karshensa zai kasance ba, ka nemi zabin Ubangiji. Domin shi ne mahaliccinka, shi ya kaddara maka dukkan abin da kake a rayuwarka, don haka ya fi kowa sanin abin da yafi zama alheri gare ka.